Hausa novels

SARKI SAMEER 2

cigaban littafin sarki sameer episode 2

💅SARKI SAMEER…. by ❤xeemat….love❤ 🌹🌹🌹Episode 2🖋🌹🌹🌹

Related Articles

Wacce Akakira da RASHEEDA tajuyo tana kallon ta itama ita take kallo tana huce takara mata magana tanace mata  bazaki wuce kidakko min ba ko shi din ubankine dazaki tsaya dan yace karkije watakon yafini matsayi awajenki ko girgiza mata kai tayi kawai sannan tayi  sum sum sum tabi ta gefansa zata wuce yayi saurin sama ta qafa tafadi qasa jikake bummmm tafadi aikwa bashiri tasaki wata qara ai bashiri tayi jifa da yarinyar da tariqe tayi saurin qarasawa gurinta tana faman cewa nashiga uku na lalace ni SADIYA ze karairayamin yarinya tafada tana qoqarin daga ta daga gun da tafadi lkacin da take wannan bambamin shiko yayi sauri yaja hannun yarinyar ya fita da ita waje yabarwa iska  ajiyarta yana jinta tana kiranshi tana zaginshi ko waiwayowa ma beyiba bare tasa ran ze amsa ko yadawo data gaji da kiran nashi kawai sai tagirgiza kai tana cewa ai zaka dawo kasameni ne tana masifa tana qoqarin ciccibar yartata amma takasa saboda itakanta nauyin kanta takeji saboda qiba ga rashin motsa jiki saide aci ajabe agu guda kamar buhun kwaki dataga bazata iyaba kawai sai itama tazauna agun tana ta faman sauke ajiyar zuciya numfaahinta harwani dan daukewa yake sabo da tsabar gajiya sai kace wacce mayunwacin zaki yabiyo aguje saida ta dan ji dama dama sannan ta bude baki da kyar tace kiyi hakuri kitashi kinji my daughter kirabu dasu zasuzone har inda nake danni  wurgice dede nake da qugun kowa bana barin ta kwana wlh sai nayi maganin su.

itadai rasheeda jinta kawai take tana kallon ta saida tagama sannan ta miqe da kyar tana shirin tafiya mom din tata tace daughter Dan Allah danzo ki tai maka min in tashi tafada tana miko mata hannu kawai saitai wani kasake tana kallonta tana tunanin ita tayama zata wani iya riqeta bayan buguwar da tayi data fadi bama wannan ba gashi ita abu ba kadan shirgegiya da ita zata wani ce mata ta dagata tabbb sai da taqara maimaita mata sannan tadawo daga tunanin da tatafi kawai sai tabe baki tace gaskiya mom bazan iyaba wlh kawai inje garin rikekii kikarasani shi inbe karyani ba aike kya Karyani  tana gama fadar haka tajuya tatafi tana qara cemata inkingaji da zaman gurin kya tashi dan kanki tai wucewarta upstairs itako da ido kawai tabita batare da tace mata komai ba inda sabo ta saba da halin diyar tata dan haka batare da taji komai aranta ba tayi qoqarin mikewa (niko nace yau naga ikon Allah mikewa kawai sai kace rakumine ze tashi) saida ta wani bubbuda qafafu sannan tayi goho da rarrafe rarrafe ta dafa bango sannan ta mike da kyar bayan ta tashinma saida ta jingina da bango ta war wara hannu dan jimm sannan tafara takawa da kyar tamu three sitter ta barbaje dan ko hauka take bazata fara tunkarar beneba tace zata hau dan tsaff zata iya runtumowa da qasa gawara tai zaman ta anan ko da daddare ta haura bayan tagama hutawa kujitafa yanzu wajen karfe biyu ko ukuma batai ba amma wai  take kiran dare😅

MUSBAHU kuwa yana fitowa da ita becemata komai ba yanufi hanyar qofar gidan su da ita yana kaita bakin wani gida da yaji jiki qofar gidan ma akarye take saboda qanqantar shima saikai tunanin ko shago ne yasakar mata hannu yajuya da nufin barin gurin sai ya tsinkayo sanyaryar muryarta me dadin sauraro wace ina tanayin magana saikaji kamar waqa take rerawa bazakaso ma tayi shiruba idan tanayi cakk ya tsaya tare da juyowa still de beyi magana ba yatsaya yana kallonta itakuma taci gaba dacewa ya musbahu nagode sosai da taimakonka sanan kuma dan Allah kakara basu hakuri wlh ba laifina shi yatsayar dani wlh kuma wlh ban….bata qarasaba yasa yatsansa akan lips dinshi alamar tai shiru kawai aikwa haka tayi sannan yace mata kar ta damu tashiga kawai kuma kar tasake tadawo gidansu ayau ko wajema karta fito tabari sai gobe zata qara magana yace kije kawai nace miki kuma kiyi abun da nafada miki kinjini da to ta amsa mishi tajuya tashiga gidan sanan shikuma yatafi yana tunanin kuma dramar dazeje yatarar wajen mahaifiyar tashi me rigimar tsaya be san meyasa batason zaman lfy ba kwata kwata arayuwar da wannan tinanin yakarasa gida har ze shiga kuma ya canza tunanin  gwarama kawai yayi wani wajen idan ta huce zuwa anjima yadawo yasan abun ze zo mishi da sauki bakamar yanzuba idan yashiga.


Tana shiga ciki tai qoqarin kawar da damuwarta saboda kar daddan ta tagane halin da take ciki saide tana shiga kuma tai karo daita tafito daga bandaki idonta kuma akanta yake har taqaraso ciki taiqasa da kanta tace dadda sannu da gida tafada tana qoqarin shigewa dakin dadda bata amsa mata ba sai cewa da tai me yasameki afuska waye yamareki haka fuskarki harta kunbura tayi ja da sauri ta shiga girgiza kai tana qoqarin mayar da hawayen da ya cika mata ido yana san zubowa tace bakomai fa dadda faduwa nayi fa tafa a qagare da son wucewa dan tagaji da tsatstsare tan datayi dadda tace hmmm naga alama ai wuce to da sauri ta wuce ciki tana shiga ta kwanta akan yar tatsitsiyar katifar dakin sannan ta fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciyar me sauraro ita sai yanzuma abun yake kara bata mata rai tanacikin yi taji muryar daddan tata akanata tanacewa tashi kizauna  ba tai mata musuba kuwa ta tashi tazauna Kai a qasa tacigaba da share hawayenta amma sunqi tsaya sam dadda ma zama tayi akusa da tare da kamota jikinta ta ungumeta saida ta bari kukan nata yadan tsagaita sannan ta dagota cike da kulawa takira sunnan ahankali tace AMEESHA ta amsa mata da na’am sanan tace fadamin abun da yafaru ahankali tafara cemata dazune mom ta aikeni gidan su hajiya Rabi ina fitowa  kuma sai na hadu da BOSSAY awaje nibanma ganshiba bafa shi yaganni yafara min magana yakirani ina zuwama nace mishi ai aunty Rasheedan bata nan sai yace ai tunda yaganni ma shikenan ko be gantaba bashi da damuwa tunda duk daya muke awajenshi sai narufe bakina ina dariya ina cewa kai kai Bossay itafa matar da za ka aurace nikuma yar aikin gidansuce taya muka zama daya da ita Kawai sai yayi murmushi shima yace to kikasani abu aduhu abakar leda ai sai anbuda za asan meye aciki ko kawai itama saitasa dariya shikuma daman abun da yakeso kenan yana so yaga tana dariya da fararen hakoranta jerarru sai yar siririyar wushirya da taqara mata mugun kyau ga kuma dimples dasuke lotsawa duk lokacin da bakinta yamotsa shide har ga Allah yarinyar tayi mishi dari bisa dari koman abun bugewa ko hassadin iza hasada yana cikin tunaninsa takatse mishi da cewa bossayn Aunty Rasheeda me kake tunanine haka murmushi yakara yi yace kemana tunaninki nake itama yar qaramar dariyar tayi fadi gsky de auntyna kake tunani ai naga yanzuma tashiga gida banga wucewarta tanan ba sai shigarta kawai nagani yace dan Allah fa tace wlh bari inje inkira maka ita yace a’a rabuda itama kawai wucewa zanyi sauri nake wlh daman abu nazo karba gurinta nayi tunanin ta dawo daga makaranta ne shiyasama ko kiranta banyiba bari wuce kicemata zanzo da daddare ta ajiyemin abun dadi yafada yanashigewa motarsa da daga mata itama tadaga mishi tanacewa zan gaya mata Allah ya kiyaye hanya yace ameen sannan yaja motarsa  yatafi itakuma ta tsaya tana murmushi dan itama harga Allah yamata yana burgeta gashi duk kudin dayake yadashi baya wulakanta mutane ga ilimi ga dukiya ga kyau ga kyawawan halaye barunshi da duniya abunsa sam baya tsokanemasa  ido saida tagama tunanin sannan tatafi cikin gidan dan tama manta da aiken da akayi mata tanashiga taji suna wannan maganar saida ta tsaya tagama ji da ta tabbatar basanan shine tashiga da nufin kan su fito tayi taqarasa aikinta ta gudu kar suhadu.

shine ko kitchen din bata qarasa ba akai mata wannan jibgar ta kwashe duk yanda abaun yafaru ta qarasa mata tare da fashewa da wani sabon kukan dadda da tagama jin abun da akayiwa jikar tata wacce takejinta harcikin ranta da dauketa kamar yar cikin ta abun yamata ciwo sosai cike da tausayinta ta fara rarrashinta da kalmomi masu dadi harsaida ta dena kukan sanan ta tashi tace mata itama taje tayi wanka tazo tayi sallah taci abinci ta kwanta ta huta idan ta tashi daga baccin zata aiketa gidan su AZEEMA aikwa cike da jin dadi ta amsa da to daman tanason zuwa gidan aminiyar tata yau kwanansu uku dayin hutun makaranta amma basu haduba ta tashi dasauri tacire kayan jikinta tafita ta dau bokitinta taje wajen yar qaramar rijiyarsu ta zura gugan da akayishi da qaramin bokitin fenti ta dibo tashiga wanka duk dadda na tsaye tana kallonta tana tausaya mata da irin wannan rayuwar da suka tsinci kansu aciki ta tafi duniyar tunani bansa me take tunaniba dan haka na kwashe komatsaina na bar gidan…


                 **
        Wacece RASHEEDA
Alhaji Alhassan Ibrahim me nasara shahararran dan kasuwa ne akasuwar kwari iyayen sama duk yan nan garin kano ne  yahadu da mahaifiyarta HALIMATUSADIYA  wace yawan cin mutane ke kiranta da sadiya  wasu kuma abayan idonta suce mata halima shirgegiya lokacin da yake kai kaya gidansu saboda gidansu irin family hause ne wanda yayi kaurin suna  inkana cikin shi kasha kallo domin gidane wanda kowa abun da yaga dama yake tsulawa gasu maguzawa abunde sai a hankali kawai  kuma ita tafara nuna mishi tanason shiko saboda tarbiyar gidansu batai mishi sai yace gaskya shi ba yanzu zeyi aure ba daga baya da tagane karya yake sai tabazama gun bokaye da malamai hartaci nasara akanshi ta aure shi yanzu haka suna da yaya uku maza biyu mace daya na farkonsu KHALID sai MUSBAHU sai autarsu RASHEEDA wacce aka shagwaba tun tana yarinya batasan daidai ba bata ba daidaiba irin yan matan nanne masu mugun rawar kai tun tana yar shekara 15 take tara samari harzuwa yanzu da take university dan ma Allah yatai maketa tadan kwaso kyaun mahaifinta da yakasance bafulatani da mom dinta dakko da anga muni kuma watakil da tarage yawan gili gili dakanta yake saboda tasan intayima ba burge mutane zataiba amma yanzude masha Allah ba laifi mutum daya ne yake iya taka mata burki tabar duk abun da take Watakon SALEEM ADAM MAGARYA  wanda ake Kira da BOSSAY  shikadai take shakka shima saboda matsanan cin son sa da Allah yadora mata awani sufa maket suka fara haduwa ya bugeta be saniba kayan hannu ta suka zube akasa tajuyo zatai mishi masifa kawai kuma saitaga yamata kwarjini takasa kawai saita tsugunna zata dauka shima ya tsugunna ze kwashe mata kawai sai suka hade hannu waje guda tare da buga goshinsu waje daya sai tai saurin mikewa tare da dafe gurin tanafadin aushhh shima sai yadago yana riqe dariyarshi.

data kusan fitowa yace “yan mata yi hakuri dan Allah ban lurabane” harara tawatsa mishi batace komai ba ganin haka yasa shi cewa “ko sai na tsugunna ne za a yafemin umm yumm sai lokacin ta dan saki murmushi tare dace eh kawai saitaga yana qoqarin tsugunnawar da tace laa wlh da wasa nake shima sai dariyar ai da sai in tsugunna yanzu de kin hakura ko kai ta daga mishi yace ok thanks tace u er well come sai yasunkuya ya kwashe mata kayan yabata tajuya kawai taje zata biya Kudin sai taje yace kubarta Kawai sai tajuya tana kallon shi da mamaki taqara juyowa tana kara mika ATM din nufin suciri kidinsu sai daya yace ai oga yace tabarshi kar ta damu ai nan gurinshi ne gabaki daya kawai sai tai tsaya takasa motsawa daga gun harya yazo dab da ita sanan yahura mata iskar bakinsa a fuskarta tadan kalleshi kadan ta kauda kai sanna ahankali ta furta mishi thanks kamar mutuniyar kirki dakansa yatayata daukan kayan suka fita har cikin motarta ya rakata ya ajiye mata a back sit sannan yadan leqa ta windo motan saboda ita harta riga da tashiga tana qoqarin tashin motar yace haka za abarni nikuma fuska adan sake tace mishi me kakeso yace komi ma inaso tadan harareshi tace bangane ba yace to ke nake nufi yafada yana zura hannusa a aljihu yadakko card dan qarami ya mika mata yace number na dan Allah in ba damuwa pls call me inkin koma gida don’t forget about me pls I swear I’m waiting for your call kinji kai ta dan kada mishi tare da cewa dont worry I will call you later in syaha Allah yace ok thank you accept me 2c I’m so happy to meet you itama tace same here tare da tayar da motar shikuma yama yana tasaniakin smile harsaida yaga tabacema ganinsa sannan yabar wajen tunda ga wannan ranar suka kulla soyayya wace acikin kaso dari nata yafi yawa tafisonshi akan yanda yakesonta wanda a yanzu jiyake gaba daya ta fitar mishi arai saboda halayenta sun fara isarshi gashi kuma har maganar aure tashiga ciki anyi magana gemu da gemu bare yace yafasa bashi da wannan damar saide hakuri
Wannan kenan
*
Wacece DADDA?
Sai munhadu agaba…
daga sabuwar marubuciyarku🖋
❤xeemat….love❤

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button

AdBlock Detected

turn off ad blocker to access this site